• Home  
  • Bayan Kaddamar Da Operation Kukan Kura Jama’a Suna Bayar Da Hadin Kai : Yan Sanda
- Babban Labari - Labarai

Bayan Kaddamar Da Operation Kukan Kura Jama’a Suna Bayar Da Hadin Kai : Yan Sanda

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ya bawa al’ummar jihar bisa hadin kai da goyon bayan da suke basu a koda yaushe don wanzar da zaman lafiya mai dorewa. cikin wani sako da kakakin rundunar yan sandan jihar Kano , SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wallafa a shafin sa na Facebook, ya ce mutane suna […]

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ya bawa al’ummar jihar bisa hadin kai da goyon bayan da suke basu a koda yaushe don wanzar da zaman lafiya mai dorewa.

cikin wani sako da kakakin rundunar yan sandan jihar Kano , SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya wallafa a shafin sa na Facebook, ya ce mutane suna basu hadin kai sosai wajen taimakawa yan sanda, musamman bayan takaddamar da Operation Kukan Kura wanda ake ta samun nasara a koda yaushe.

A cewarsa acan baya sun taba kaddamar da Operation Puff Adder wato kan kace Kobo, kuma shima jama’a sun bayar da hadin kai sosai, sai dai ya ce a wannan lokaci hadin kan da ake samu yafi na baya.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000