Tag: Kano

Labarai

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama wanda ake zargi da damfarar mutane da cewa shi babban jami’in Dan sandan ne.

Rundunar yan sandan jihar Kano ta kama wani matashi mai shekaru 35, Adamu Musa, bisa zargin yin karyar cewar shi, babban jami’in ’yan sanda da kuma damfarar jama’a da sunan samar musu da aikin ’yan sanda da sauya wurin aiki. An kama Adamu, mazaunin Kureken Sani Quarters a Kano, a ranar 1 ga Satumba 2026, […]

Babban Labari Labarai

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.

Rundunar ƴansandan Jihar Kano ta sanar da daukar tsauraran matakan tsaro domin tabbatar da zaman lafiya yayin bikin Takutaha na shekarar 2026, wanda za a gudanar a ranar Talata, 1 ga Satumba. Kwamishinan ’yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya yabawa al’ummar jihar bisa yadda suke gudanar da bikin cikin lumana, hadin kai da […]

Labarai

Rimingado ya kaddamar da kwamitoci 9 da kan yaki da miyagun kwayoyi a Kano.

Shugaban kwamitin haɗin gwiwar hukumomi ta yaƙi da shaye-shaye da fataucin miyagun kwayoyi a Kano, Muhuyi Rimingado, ya ƙaddamar da kwamitoci tara domin ƙara ƙaimi wajen yaƙi da matsalar miyagun ƙwayoyi a jihar. Rimingado ya buƙaci mambobin kwamitocin da su kasance masu jajircewa, tare da aiki kafada da kafada wajen ganin an cimma manufofin rundunar. […]

Labarai

Miyagun kwayoyi: NDLEA ta kama mutum 80 a Kano

A mako guda, Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kama mutum 80 tare da watsa maboya 16 na masu ta’ammali da miyagun kwayoyi a Jihar Kano. Hukumar ta fara samamen, mai suna “Operation Restore Order” ne daga ranar 10 zuwa 16 ga watan nan na Agusta, inda ta kai farmaki […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai