Home » Gobara ta Tashi a Kotun Ƙolin Najeriya

Gobara ta Tashi a Kotun Ƙolin Najeriya

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

A cigaba da kawo muku labari game da gobarar da ta tashi a kotun ƙolin Najeriya da ke Abuja a yau.

Shugaban Hukumar agajin gaggawa a Babban Birnin Tarayya, Abbas Idris, ne ya tabbatar wa da majiyarmu da faruwar lamarin, inda ya ce tuni jami’an kai ɗauki suka isa harabar kotun.

Sai dai ya tabbatar da cewa wutar ta shafi wani ɓangare ne kawai na kotun.

A cewarsa: ofisoshi biyu ne lamarin ya shafa kuma babu wanda ya rasa ransa a yayin gobarar.

Ya ƙara da cewa yanzu haka jami’an kai ɗauki sun samu nasarar shawo kan wutar.

Bayanan farko-farko da ke fitowa dai sun nuna cewa wutar lantarki ne ya haddasa gobarar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?