EFCC Na Ƙoƙarin Daƙile Muradin Malami Na Yin Takarar Gwamna — ADC

Jam’iyyar ADC ta zargi Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC) da amfani da siyasa wajen belin tsohon Ministan Shari’a na Tarayya, Abubakar Malami (SAN).

Jam’iyyar ta ce babu wata shaida da ke nuna cewa Malami ya karya sharuɗan belin da aka ba shi.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran jam’iyyar na ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta ce an ɗauki matakin ne jim kaɗan bayan Malami ya halarci wani taron siyasa a Jihar Kebbi.

Jam’iyyar ta ce matakin da aka ɗauka ya nuna yadda aka ƙulla wani abu domin daƙile burinsa na takarar gwamna, ba wai domin neman adalci ba.

“Jam’iyyar ADC na kallon soke belin Malam Abubakar Malami da EFCC ta yi a matsayin amfani da siyasa,” in ji Abdullahi.

“Daga dukkanin bayanan da muka samu, Malami bai karya ko ɗaya daga cikin sharuɗan belin da aka ba shi ba, kuma hana belin ya sanya alamar tambaya a kan manufar EFCC.”

ADC ta ce tana goyon bayan yaƙi da cin hanci da rashawa tare da mara wa EFCC baya wajen gudanar da aikinta.

Sai dai jam’iyyar ta yi gargaɗin cewa ɗaukar matakai na ɓangare ɗaya kan ‘yan adawa na iya rage amincewar jama’a da kuma raunana sahihancin yaƙi da cin hanci a ƙasar.

Jam’iyyar ta kuma ce babu wata hukuma ta gwamnati da ke da ikon hana ɗan ƙasa shiga harkokin siyasa ba tare da umarnin kotu ba.

Ta ƙara da cewa tana tare da Malami, tare da yin kira da a sake nan take ba tare da sharuɗan da za su taƙaita masa haƙƙinsa na siyasa ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *