Tag: Nigeria

Babban Labari

‎Gwamnatin Katsina ta ce jami’a su kwantar da hankalinsu, yayin da ‘yan bindiga suka nemi shanu 700 da Tumaki 1,000.

Fargaba ta mamaye jihar Katsina yayin da ‘yan bindiga suka bukaci a ba su shanu dari bakwai (700) da tumaki dubu (1,000) daga wasu al’umma, tare da bayar da wa’adin kwanaki shida, lamarin da ya tilasta wa mazauna yankunan tserewa ‎ ‎Mazauna wasu kauyuka a Karamar Hukumar Kankia ta Jihar Katsina sun shiga cikin tsananin […]

Babban Labari

Hukumar NOA da ƙungiyar NAWOJ sun jaddada muhimmancin wayar da kan jama’a gabanin zaɓe

Hukumar wayar da kai ta ƙasa NOA tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da ƙungiyar mata ƴan jarida ta ƙasa NAWOJ, sun jaddada aniyarsu na ci gaba da ilimantar da mutane don inganta kyawawan ɗabi’u, da sanya kishin ƙasa,  gabanin zaɓen 2027. Babban Daraktan NOA, Mallam Lanre Issa-Onilu, ya bayyana hakan inda ya ce wannan haɗin […]

Babban Labari

Gwamnati Ta Fitar Da Sunan Mutum 48 Da Ake Zargi Da Ɗaukar Nauyin Ta’addanci A Najeriya

Gwamnatin Tarayya, ta fitar da sunan mutane da ƙungiyoyi 48 waɗanda ake zargi da tallafa wa ayyukan ta’addanci a faɗin Najeriya. Hukumar da ke sanya takunkumi ta Najeriya (Nigeria Sanctions Committee) ce, ta bayyana jerin sunayen a ranar Asabar, 11 ga watan Afrilu, 2026. Sunayen ya ƙunshi ɗaiɗaikun mutane da ƙungiyoyin da bincike ya nuna […]

Babban Labari

Ƙaramar ministar ƙwadagon Najeriya ta yi murabus

Ƙaramar Ministar kwadagon Najeriya Nkeiruka Onyejeocha ta yi murabus daga muƙaminta. Ta sanar da murabus ɗin nata ne a shafinta na X, inda ta miƙa godiyarta ga shugaba Bola Ahmed Tinubu wanda ya bata dama ta yi aiki da gwamnatinsa. Ta bayyana ajiye muƙamin nata a matsayin matakin rufe wani gagarumin babi na rayuwarta a […]

Babban Labari

Tarko INEC ke son ɗana mana kuma ba za mu kamu ba – ADC

Jama’iyyar adawa ta ADC ta haɗakar ƴan adawar Najeriya ta zargi hukumar zaɓen ƙasae INEC ta naɗa mata tarko ta hanyar hanyar yunƙurin dakatar da ita daga gudanar tarukanta domin zaɓen shugabanninta. ADC – tsagin David Mark – ta jaddada aniyar ci gaba da tsare-tsarenta na gudanar da zaɓukan shugabanninta na jihohi da babban taron […]

Babban Labari

Tinubu ya gana da shugaban Chadi

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙucnin shugaban Chadi Idriss Déby a ranar Alhamis. Sun yi ganawar ce cikin sirri a fadar shugaban Najeriya da ke Abuja, inda ake sa ran sun tattauna kan batutuwa da suka shafi tattalin arziki da kuma haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen biyu. Ganawar na zuwa ne kafin tafiyar shugaba […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai