Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da naɗa wasu ƙarin mutane biyar mukamai daban-daban.
Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da Sakataren yada labaran gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanya wa hannu
Wadanda aka naɗa sun haɗa da:
1. Engr. Garba Ahmed Bichi
Manajan Daraktan Hukumar Ruwa ta Jihar Kano
2. Dr. Rahila Mukhtar
Sakatariyar Hukumar Kula da Taimakekeniya Lafiya ta Jihar Kano (KCHMA).
3. Hassan Baba Danbaffa
Daraktan Hukumar Kula da Tituna ta Jihar Kano (KARMA).
4. Arc. Ibrahim Yakubu
Daraktan Hukumar Tsara Birane ta Jihar Kano (KNUPDA).
5. Abdulkadir Abdussalam
Akanta Janar na Jihar Kano
Sanarwar ta ce nan ba da jimawa ba za a sanar da lokacin da za’a rantsar da wadanda aka nada domin ba su damar sauke nauyin da aka dora musu nan take.