Home » Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Ƙwadago Za Su Yi Wani Zama Kan Batun Cire Tallafin Mai

Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Ƙwadago Za Su Yi Wani Zama Kan Batun Cire Tallafin Mai

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Ƙwadago Za Su Yi Wani Zama Kan Batun Cire Tallafin Mai
­­­A yau ake sa ran wakilan gwamnatin tarayya za su yi wani zama na musamman da shuwagabannin ƙungiyar ƙwadago da misalin ƙarfe 2 na rana.

Wannan zama dai za a yi shi ne game da cire tallafin man fetur da gwamnatin Bola Ahmad Tinubu ta tabbatar bayan ayyana hakan da Gwamnatin Shugaba Buhari ta yi.

Wannan tabbaci ya fito ne daga bakin shugaban ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa Joe Ajaero a yayin hirarsa da gidan talabijin na Channels.

Sannan ya tabbatar da cewa a daren jiya ne, jami’an sabon gwamnatin suka tuntuɓe shi domin tabbatar da wannna zama.

Ya ce matsayar ƙungiyar shi ne, idan har shugaba Tinubu na da niyya mai kyau game da cire tallafin man fetur, to wajibi ne ya samar da wata hanya da za a waraware matsalar da hakan ka iya jawowa.

Cikin abubuwan da shugaban ƙwadagon ke sa ran gwamnatin za ta samar akwai farfaɗo da matatun mai guda huɗu na ƙasar nan da samar da hanyar zirga-zirga ta yau da kullum ga ma’aikata.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?