Da yammacin ranar Litinin 12 ga watan Disamba ne ɗaliba makarantar St Mary’s da ke Papiri a jihar Neja suka isa gidan gwamnati bayan an sanar da samun nasarar ceto su.
Sai dai har yanzu babu tabbacin ko an biya kuɗin fansa ko ba a biya ba.
Daga cikin waɗanda suka tarbe sun haɗa da Gwamnan Neja, Umaru Bago da shugabannin ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya da kuma shugabannin makarantar.


