Home » Borno: NNPC Ta Sha Alwashin Cigaba da Laluben Ɗanyen Man Fetur

Borno: NNPC Ta Sha Alwashin Cigaba da Laluben Ɗanyen Man Fetur

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
NNPC Ta Sha Alwashin Cigaba da Laluben Ɗanyen Man Fetur a Jihar Borno

Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya lashi aniyar cigaba da laluben danyen man fetur a yankin tafkin Chadi.

Kanfanin zai koma Maidugurin ne a  cikin mako mai zuwa bayan shekaru 5 da dakatar da aikin sakamakon mummunan ayyukan kungiyoyin ‘yan ta’adda.

Malam Mele Kyari shugaban kamfanin na NNPC, ya bayyana cewa matakin komawa ci gaba da laluben man a jihar Borno wani umarni daga shugaban ƙasa mai barin gado Muhammadu Buhari.

Wannan yunƙuri dai na zuwa ne bayan gano danyen man fetur da aka yi a jihohin Gombe da Bauchi a watan Nuwamba da jihar Nassarawa.

Wannan dalili ya haifar da ɗaura aniyar ganin an cigaba da laluben man da ke jihar Borno cikin kalaman na Mele Kyari.

Don haka, ya tabbatar da cewa, Ma’aikatar za ta tabbatar da samar da tsaro ga ma’aikatanta da za su yi aiki a yankin tafkin Chadi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?