Tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya, Sanata Ovie Omo-Agege ya fice daga Jam’iyyar APC mai mulki.
Cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara ka harkar labarai, Sunday Areh ya fitar, Sanata Omo-Agege ya ce ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓa da ya yi da makusantansa a siyasa da kuma magoya bayansa, bugu da ƙari kuma abubuwan baya-baya da suka faru a jam’iyyar reshen jihar Delta.
Tsohon ɗanmajalisar ya ce ya fi dacewa ya nemi cika burinsa na siyasa da muradan da yake da shi ga al’ummar mazaɓarsa a wata jam’iyyar inda ya ƙara da cewa ba zai ci gaba da kasancewa a jam’iyyar da ba zai iya samar da ci gaba ga mutanensa ba.
Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito Omo-Agege yana gode wa APC bisa damar da ta ba shi na riƙe muƙamin mataimakin shugaban majalisar dattawa a majalisa ta tara inda kuma ya ce yana yi wa jam’iyyar fatan alheri.
