Home » Sarkin Musulmi Ya Miƙa Saƙon “Easter” Ga Shugaban CAN

Sarkin Musulmi Ya Miƙa Saƙon “Easter” Ga Shugaban CAN

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

A cikin wani saƙon taya murna na bukin Easter da Sarkin Musulmi ya aika wa shugaban Ƙungiyar Kiristocin Najeriya, Daniel Okoh, ya ce rashin fahimta tsakanin addinan biyu, a matsayin ‘aikin Shaiɗan ne,’ kamar yadda Alƙur’ani ya bayyana.

A cikin jawabin nasa, wanda ya samu sa hannun Mataimakin shugaban Majalisar Ƙolin Lura da Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya, Farfesa Salisu Shehu, Sarkin Musulmin ya buƙaci shugaban na CAN da ya haɗa hannu da Masarautar wajen ganin an rage yadda limamai da fastoci ke cusa wa mabiyansu ƙiyayya ta siyasa da kuma munanan kalamai.

Daga ƙarshe mai alfarma Sarkin Musulmi ya taya al’ummar Kirista murnar zagayowar ranar Easter tare da addu’ar samun cigaban Najeriya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?