Tsohon sakataren gwamnatin Najeriya, Babachir Lawal ya ce babban dalilin da ya sa ya bi haɗakar ƴan hamayya a ƙasar shi ne “rashin jin shawarwarin” da shi da kuma sauran ƴan Najeriya ke bai wa shugaban ƙasar Bola Tinubu.
Babachir na cikin ƴan siyasar Najeriya masu hamayya da suka fi jan hankali bayan ganin su cikin waɗanda suka ja tunga suka dunƙule domin samar da jam’iyyar da za ta ƙalubalanci shugaba Tinubu a zaɓen shekara ta 2027.
Ƴan adawar sun zargi gwamnatin Tinubu da gazawa wajen biyan buƙatun al’ummar ƙasar, duk da cewa wasu na ganin cewa ya yi wuri a yanke hukunci.
A tattaunawarsa da BBC tun bayan ayyana jam’iyyar ADC da ƴan hamayyar suka yi a matsayin lemarsu, Lawal ya zargi Tinubu da yanke hukunci kan manufofi masu gagarumin tasiri ba tare da shawartar masana ba.
“Janye tallafin mai (fetur) da ya yi bai yi tunani a kai ba, da zaman sa shugaban ƙasa cikin minti ɗaya ya janye tallafi, ba ya da minista, ba ya da kowa, shi kaɗai ya janye,” in ji Babachir.
- Sojojin Najeriya Sun Kashe Mayaƙan Boko Haram 24
- Yan Sanda Sun Kaddamar Da Operation Kukan Kura Tare Da Kama Mutane 98 A Kano
Bola Tinubu ya janye tallafin man fetur ne a ranar 29 ga watan Mayun 2023 lokacin jawabin karɓar mulki a matsayin sabon shugaban Najeriya.
Ana kallon janye tallafin a matsayin ɗaya daga cikin manufofin shugaban ƙasar da suka haifar da tsadar rayuwa da tashin farashin kayan masarufi, wani abu da har yanzu al’ummar ƙasar ke kokawa a kai.
Sai dai Tinubu ya ce ya yi hakan ne domin rage kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa wajen biyan tallafin waɗanda za a iya amfani da su domin ayyukan ci gaban ƙasa, tare da cewa za a ga amfanin matakin a nan gaba.

