Barazana Ta Tunkaro Kananan Hukumomin Najeriya 774
Kananan Hukumomi 774 na fadin Najeriya na fuskantar barazanar rasa samun kudadensu na wata-wata kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.
Kananan Hukumomi 774 na fadin Najeriya na fuskantar barazanar rasa samun kudadensu na wata-wata kai tsaye daga asusun gwamnatin tarayya.
Gwamnatin Najeriya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ta ce za ta ɗauki mataki a kan jihohin da suka ƙi gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi da ake sa ran zai tabbatar da cin gashin kai na ƙananan hukumomin kamar yadda kotun ƙolin ta zartar a kwanakin baya.
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta ce babu fashi dangane da gudanar zaɓen ƙananan hukumomin jihar da ke tafe ranar Asabar mai zuwa.