Home » Ƙasar Saudiyya Ta Ja Kunnen Masu Ɗaukar Hoto a Lokacin Ibada

Ƙasar Saudiyya Ta Ja Kunnen Masu Ɗaukar Hoto a Lokacin Ibada

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar kula da aikin Haji da Umrah ta Saudiyya ta yi kira ga masu ziyarar ibada da su guji ɗauke-ɗauken hotuna a yayin gudanar da ibada a wurare masu alfarma.

Hukumar ta ce bai kamata masu ziyarar ibadar su ɓige da ɗaukar hotuna ba a maimakon mayar da hankali kan ibadar da ta kai su ƙasar.

Haka kuma hukumar ta gargaɗi masu ɗaukar hotunan da su guji ɗaukar hoton da fuskokin mutane a cikin hoton nasu ba tare da izini ba.

Sannan ta bayyana cewar masu ziyarar ibadar su daina tsayawa don ɗaukar hoto a wuraren da jama’a da dama ke taruwa, domin a cewarta hakan na janyo cunkuson jama’a a wuraren.

A baya-bayan nan dai mutane sun ɓullo da salon ɗaukar hotuna a lokacin ziyarar Umrah ko Aikin Hajji tare da wallafawa a shafukansu na sada zumunta.

Lamarin da wasu malamai ke ganin cewa yawan yin hakan ka iya zama ‘Riya’, abin da kuma a cewar malaman zai iya ɓata wa mutane niyyar ibadar tasu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?