Daga : Safiyanu Haruna Kutama
Fitaccen malamin addinin Islama da ke Jihar Bauchi, Dokta Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi ya riga mu gidan Gaskiya.
Makusantan malamin sun tabbatar da rasuwarsa , Inda ya shafe tsawon lokaci Yana karantarwa da kuma harkar kasuwanci.
Malamin ya yi fama da rashin lafiya inda gabanin watan Ramadana ya fita neman magani a ƙasashen Masar da Saudiyya.
Za a yi jana’izarsa da ƙarfe 10 na safiyar Jumu’a a Masallacin Idi na Games Village da ke Jihar Bauchi.