• Home  
  • Yan Najeriya Sun Kusa Fara Shan Wutar Sa’o’i 24 — Minista
- Babban Labari - Labarai

Yan Najeriya Sun Kusa Fara Shan Wutar Sa’o’i 24 — Minista

Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya ce nan ba da jimawa ba Najeriya za ta fara samun wutar lantarki ta tsawon sa’o’i 24 ba tare da ɗaukewa ba. Ya bayyana haka ne a Abuja lokacin da ya ƙaddamar da sabbin ɗakunan horo da ɗakin kwana a Cibiyar Horas da Ma’aikata ta Ƙasa (NAPTIN). Adelabu, ya […]

Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, ya ce nan ba da jimawa ba Najeriya za ta fara samun wutar lantarki ta tsawon sa’o’i 24 ba tare da ɗaukewa ba.

Ya bayyana haka ne a Abuja lokacin da ya ƙaddamar da sabbin ɗakunan horo da ɗakin kwana a Cibiyar Horas da Ma’aikata ta Ƙasa (NAPTIN).

Adelabu, ya ce gwamnati ta samu nasarar samar da wutar lantarki da rarraba ta a matakin da ba a taɓa samu ba a tarihin ƙasar.

Ya bayyana cewa bunƙasa wutar lantarki shi ne ginshiƙin ci gaban ƙasa, domin tana tallafa wa makarantu, asibitoci, masana’antu da kasuwanci.

Ya ƙara da cewa Najeriya na da ƙwarewa da ma’aikatan da za su iya ƙera mita, na’urar rarraba wuta da wayoyin lantarki a cikin gida domin dogaro da kai.

Sabbin gine-ginen da aka samar a NAPTIN za su taimaka wajen bai wa matasa damar samun ƙwarewa wajen inganta harkar wutar lantarki.

Ƙungiyar Tarayyar Turai (EU) da Gwamnatin Faransa ne suka tallafa da kuɗi da kuma shirye-shiryen horaswa.

EU, ta kuma bayar da tallafin Yuro miliyan 100 domin bunƙasa makamashi a Najeriya, wanda zai ƙara yawan megawat 400 nan da 2027, wanda zai amfanar da mutum sama da miliyan biyar.

Masana sun ce wannan zai ƙara samar da ayyukan yi tare da rage dogaro da man fetur.

Daraktan NAPTIN, Ahmed Nagode, ya ce wannan aiki wata sabuwar hanya ce ta samar da makoma mai kyau.

Ya kuma bayyana cewa haɗin gwiwa da ƙasashen waje zai bai wa matasan Najeriya damar koyon sabbin dabaru da shugabanci a fannin makamashi.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai