• Home  
  • Gwamnan jihar Jigawa Mallam Umar Namadi Ya rage lokacin aikin ga ma’aikata Saboda azumi
- Babban Labari - Labarai

Gwamnan jihar Jigawa Mallam Umar Namadi Ya rage lokacin aikin ga ma’aikata Saboda azumi

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da rage lokutan aiki ga ma’aikatan gwamnati a lokacin azumin watan Ramadan. ‎ ‎Gidan Rediyon Jihar Jigawa ya rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Shugaban Ma’aikatan Jihar, Muhammad K Dagaceri, ya sanyawa hannu a ranar Laraba 18 ga Fabrairu 2026. ‎ ‎Sanarwar ta ce bisa sabon […]

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da rage lokutan aiki ga ma’aikatan gwamnati a lokacin azumin watan Ramadan.

‎Gidan Rediyon Jihar Jigawa ya rawaito cewa, wannan na cikin sanarwar da Shugaban Ma’aikatan Jihar, Muhammad K Dagaceri, ya sanyawa hannu a ranar Laraba 18 ga Fabrairu 2026.

‎Sanarwar ta ce bisa sabon tsarin, ma’aikata za su rika zuwa aiki daga karfe tara na safe zuwa karfe uku na rana a ranakun Litinin zuwa Alhamis, maimakon karfe biyar na yamma.

‎A ranar Juma’a kuma, za su rika zuwa aiki daga karfe tara na safe zuwa karfe ɗaya na rana.

‎Muhammad K Dagaceri ya ce an hakan ne domin saukaka wa ma’aikata Musulmi tare da ba su damar samun isasshen lokaci domin gudanar da ibadu da sauran ayyukan alheri a cikin watan mai alfarma.

‎A ƙarshe, sanarwar ta bukaci ma’aikata su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’o’i domin samun zaman lafiya da bunkasar tattalin arzikin jihar da kasa baki daya.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000