Tag: jigawa

Babban Labari

Jami’ar Sule Lamido ta ziyarci tashar MUHASA kan shirin bude sashen koyar da aikin jarida

Wakilai daga Jami’ar Sule Lamido da ke Kafin Hausa sun kai ziyara tashar MUHASA Radio da Talabijin, a wani mataki na ƙoƙarin buɗe sashen koyar da aikin jarida a jami’ar. Farfesa Mustapha Dan Malam ne ya jagoranci tawagar, inda suka gana da shugabanci da ma’aikatan tashar domin tattauna muhimman batutuwan da suka shafi koyar da […]

Babban Labari

Jigawa na da ƙarfin samar da sama da kashi 50 cikin 100 na buƙatar shinkafar Najeriya – Shugaban NUJ

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Jarida ta Najeriya (NUJ), Kwamared Alhassan Yahaya, ya yi kira ga gwamnonin jihohin Najeriya su yi koyi da yadda Gwamnatin Jihar Jigawa ke zuba jari a fannin noma da sauran harkokin samar da arziki, domin magance matsalar ƙarancin abinci da samar da ayyukan yi. Shugaban NUJ ya yi wannan kiran ne a […]

Babban Labari

Majalissar Zartarwa ta amince da gina sabuwar fadar Sarkin Dutse kan Biliyan 2.77

Majalisar Zartarwar Jihar Jigawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Umar A. Namadi, FCA, ta amince da jerin manyan tsare-tsare, kwangiloli da shirye-shiryen ci gaba da za su inganta sufuri, noma, ilimi, samar da ruwa, da kuma bunƙasa tattalin arzikin jihar. Ɗaya daga cikin manyan matakan da majalisar ta ɗauka shi ne amincewa da sanya hannu kan […]

Babban Labari

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Gwamnatin Jihar Jigawa ta bayyana cewa ta kashe kusan Naira bakwai (7) a karkashin Shirin Tallafa wa Ma’aikatan Gwamnati ta Fuskar Noma (JSWAP), inda sama da ma’aikatan gwamnati 17,000 suka ci gajiyar shirin tun daga mataki na farko zuwa na uku. An bayyana hakan ne yayin kaddamar da rabon kayan aikin noma na kashi na […]

Babban Labari

Gwamnatin Jigawa ta ƙara mafi ƙarancin fansho zuwa N20,000, ta ware sama da N9bn don ayyuka 

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da ƙara mafi ƙarancin kuɗin fansho daga Naira 12,000 zuwa Naira 20,000 a kowane wata ga tsofaffin ma’aikatan gwamnati da na ƙananan hukumomin jihar. A cewar Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Sagir Musa Ahmed, gwamnatin za ta kashe sama da Naira biliyan biyu a duk shekara […]

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai