Majalisar dokokin Najeriya ta ɗage zamanta zuwa ranar 5 ga watan Maris mai kamawa.
Tun da farko an tsara majalisar za ta koma zama ranar 24 ga watan Fabrairu.
Sai dai cikin wata sanarwa da akawun majalisar, Kamoru Ogunlana ya fitar, ya ce majalisar ta ɗage komawar ne domin bai wa kwamitocinsa damar kammala ayyukan da ke gabansu na kare kasafi.

