• Home  
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Sanya Dokar Zaman Gida na Awa 24
- Labarai

Gwamnatin Jihar Kano Ta Sanya Dokar Zaman Gida na Awa 24

Gwamnatin Jihar Kano Ta Sanya Dokar Zaman Gida na Awa 24

Gwamnatin jihar Kano, ta bakin kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Muhammad Garba, ta sanar da sanya dokar zama a gida na daga safiyar wannan rana zuwa dare.

Wannan na zuwa ne jim kaɗan bayan sanar da sakamakon zaɓen gwamna na jihar Kano da hukumar zaɓe ta yi tare ayyana Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Ya ce wannan mataki ne da aka  ɗauka domin magance yiwuwar ɓarkewar tashe-tashen hankula a jihar.

Sai dai har izuwa yanzu al’umma na cigaba da fitowa da yawo kan tituna domin bayyana farin cikinsu game da nasarar da Abba Kabir Yusuf ya samu.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai