• Home  
  • Ranar Tunawa Da Larurar Shanyewar Ɓarin Jiki
- Labarai

Ranar Tunawa Da Larurar Shanyewar Ɓarin Jiki

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ware duk ranar 29 ga watan Oktoba na kowacce  shekara a matsayin ranar tunawa da ciwon shanyewar barin jiki.

DAGA: YASIR ADAMU

Hukumar lafiya ta duniya WHO ta ware duk ranar 29 ga watan Oktoba na kowace  shekara a matsayin ranar tunawa da ciwon shanyewar barin jiki.

Taken ranar bana  shi ne Together we are Greater Than Stroke wato Mu Haɗu Mu Yaƙi Shanyewar Ɓarin Jiki Tare.

Albarkacin ranar Muhasa Radio ya yi duba na tsanaki game da wannan cuta ta shanyewar barin jiki inda wakilinmu Yasir Adamu ya leka asibitoci kuma ya samu zantawa da masu lalurar shanyewar ɓarin jikin da kuma likitan da ke lura da irin wannan ciwo.

Ya fara ne da farko da ziyartar  asibitin ƙwararru na Murtala da ke ƙwaryar birnin Kano inda na yi katarin samun Dokta Aliyu Dausayi wanda ya yi karin haske kan abubuwan da suke jawo wa mutum  kamuwa da cutar shanyewar barin jiki.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai