Home » Adadin Mutanen Da Suka Rasu A Majia Sun Ƙaru Zuwa 180.

Adadin Mutanen Da Suka Rasu A Majia Sun Ƙaru Zuwa 180.

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Tun bayan Iftila’in haɗarin Tankar mai da ya faru a ranar Talata a Majiya dake Jihar Jigawa, zuwa yanzu adadin mutanen da suka rasu sun kai 180 a cewar wasu mazauna yankin.

Tun a ranar 15 ga watan Oktoba ne wata babbar tankar dakon man fetur tayi haɗari akan hanyar ta ta zuwa Jihar Yobe da ga Kano.

Haɗarin ya faru ne a Majiya dake ƙaramar hukumar Taura a Jihar Jigawa.

Inda nan take aka tabbatar da rasuwar kimanin mutane 150, sai kuma ƙarin wasu da suka jikkata.

Jihar dai na ta samun tallafi, a baya bayan nan.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?