Home » Gwamnonin Arewa Sun Tallafawa Jihar Jigawa Da Naira Miliyan 950

Gwamnonin Arewa Sun Tallafawa Jihar Jigawa Da Naira Miliyan 950

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Ƙungiyar gwamnonin Arewa ta bayar da gudunmawar Naira Miliyan 950 don taimakawa iyalan waɗanda suka rasu dama waɗan da suka jikkata sakamakon faɗuwar tankar dakon man fetur a Majia jihar Jigawa.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewacin Najeriya gwamna Muhammad Inuwa Yahaya na jihar Gombe ne ya sanar da ba da tallafin ya yin ziyarar da su ka kai don Jajantawa gwamnati dama al’ummar Jihar.

Jama’a daga da wajen Najeriya na cigaba da jajantawa al’ummar jihar Jigawa faruwar wannan ifti’ai.

A kwanakin baya ma dai al’ummar ƙauyen Nahuche da ke ƙaramar Hukumar Taura sun fuskanci ifti’ain ambaliyar ruwa da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

  • Jihar Jigawa na ɗaya daga cikin jihohin da ke da zaman lafiya a Arewacin Najeriya, sai dai a bana an samu mace-mace da dama sakamakon ifti’ai iri daban-daban.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?