Home » An Yi Jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi

An Yi Jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi

Dubban Mutane daga sassan Najeriya ne suka Halarci Jana’izar Shaik Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi wanda Allah ya yi wa rasuwa a daren  Alhamis.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga Safiyanu Haruna Kutama

Dubban Mutane daga sassan Najeriya ne suka Halarci Jana’izar Shaik Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi wanda Allah ya yi wa rasuwa a daren  Juma’a.

An gudanar da Jana’izar ne a Masallacin idi na Game Village dake garin Bauchi.

Shaik Abdul’aziz Idris Dutsen Tanshi dai ya rasu yana da Shekaru 68.

ya bar ‘ya’ya 38 da jikoki da Dama Kuma matan sa 3.

Manyan Yan siyasa irin su tsohon matemakin shugaban Nigeriya Atiku Abubakar da kungiyar Jama’atul Izalatul Bidi’a Wa’iqamatus Sunna JIBWIS da sauran manyan malamai tuni suka fara aikewa da sakon ta’aziyya tare da alhinin rasuwar sa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?