Home » Kotu Ta Sauke Julius Abure Daga Shugabancin Jam’iyyar LP

Kotu Ta Sauke Julius Abure Daga Shugabancin Jam’iyyar LP

Kotun Ƙoli ta soke hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja, ta yanke wanda ya amince da Julius Abure a matsayin shugaban jam’iyyar LP na ƙasa.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Kotun Ƙoli ta soke hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja, ta yanke wanda ya amince da Julius Abure a matsayin shugaban jam’iyyar LP na ƙasa.

A ranar Juma’ar nan ce jaridar Aminiya ta ruwaito cewa, wani kwamitin alƙalai biyar na Kotun Ƙoli, ya ce Kotun Ɗaukaka Ƙara ba ta da hurumin yanke hukunci kan shugabancin jam’iyyar.

Alƙalai sun bayyana cewa batun shugabanci al’amari ne da ya shafi cikin jam’iyya, kuma ba kotu ke da ikon yanke hukunci a kai ba.

Kotun ta kuma ce wa’adin mulkin Julius Abure a matsayin shugaban jam’iyyar ya ƙare tun da farko.

Kotun ta amince da ƙarar da Sanata Ester Nenadi Usman da wani mutum suka shigar.

Sai dai ta yi watsi da ƙarar da ɓangaren Abure ya shigar, inda ta bayyana cewa ba ta da amfani.

Wannan hukunci na shugabancin Julius Abure a matsayin shugaban jam’iyyar LP ya ƙare hukumance.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?