Home » An Zaɓi Alhaji Muhammad Babandede OFR Shugaban Majalisar Zartarwar NBMOA

An Zaɓi Alhaji Muhammad Babandede OFR Shugaban Majalisar Zartarwar NBMOA

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Mamallakin tashoshin rediyo da talabijin na MUHASA Alhaji Muhammad Babandede OFR, ya zama Shugaban Majalisar Zartarwar Kungiyar Masu Gidajen Rediyo Da Talabijin Masu Zaman Kansu Na Arewacin Najeriya. 

Wannan zaɓe na ƙunshe a cikin wata takarda ta musamman da Shugaban Majalisar Amintattu na ƙungiyar Alhaji Dokta Ahmed Tijjani Ramalan ya sanya wa hannu.

Shugaban Majalisar Amintattun ƙungiyar ta NBMOA ya ce Alhaji Muhammad Babandede OFR zai riƙe wannan muƙami ne an tsawon watanni 6.

Inda ake sa ran a zamansa na shugabancin wannan ƙungiya zai gudanar da zaɓen cike guraben da ake da su.

Dokta Ramalan ya ce suna sa ran gogewar Alhaji Muhammad Babandede zai taimakawa ƙungiyar zuwa tudun mun tsira.

Ya kuma bayyana cewa suna da yaƙinin Alhaji Babandede zai samarwa ƙungiyar ‘yanci da mutunci a idon duniya.

Takardar ta bayyana cewa Alhaji Muhammad Babandede OFR zai shiga ofishinsa a matsayin shugaban majalisar zartarwar ƙungiyar daga ranar 1 ga watan Disamba, 2024.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?