• Home  
  • Yan Sanda Dubu 45,000 Ne Za Su Kula Da Zaben Jihar Anambra
- Babban Labari - Labarai

Yan Sanda Dubu 45,000 Ne Za Su Kula Da Zaben Jihar Anambra

Babban Sifeton ƴansandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya amince da aika jami’an ƴansanda 45,000 domin bayar da tsaro a lokacin zaɓen gwamnan jihar Anambra da za a yi ranar 8 ga watan Nuwamban 2025. Egbetokun – wanda kwamishinan ƴansanda mai lura da dakarun kai ɗaukin gaggawa – ya bayyana hakan ne ranar Talata a lokacin wata […]

Babban Sifeton ƴansandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya amince da aika jami’an ƴansanda 45,000 domin bayar da tsaro a lokacin zaɓen gwamnan jihar Anambra da za a yi ranar 8 ga watan Nuwamban 2025.

Egbetokun – wanda kwamishinan ƴansanda mai lura da dakarun kai ɗaukin gaggawa – ya bayyana hakan ne ranar Talata a lokacin wata ganawa da kwamitin haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da aka gudanar a shalkwatar hukumar zaɓen ƙasar da ke Abuja.

Babban Sifeton ƴansandan ya ce jami’an da za a tura za su tabbatar da tsaro a kafin zaɓen da lokacin zaɓen da ma bayan zaɓen.

Ya ƙara da cewa za a fara tura jami’an ne tun daga ranar 1 ga watan Nuwamba domin kawar da duk wata barazana ga zaɓen.

Egbetokun ya kuma ce baya ga jami’an ƴansanda akwai sauran hukumomin tsaro da za su taka rawa a zaɓukan da suka haɗa da na farin kaya, DSS da rundunar tsaron fararen hula da sibil difens da sojoji.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000