Sojojin Sun Kwace Ikon Fadar Shugaban Kasar Sudan
Rundunar Sojin Sudan ta bayyana cewa ta sake ƙwace iko da fadar shugaban ƙasar da ke Khartoum a ranar Juma’a bayan gwabza yaƙi da rundunar RSF.
Rundunar Sojin Sudan ta bayyana cewa ta sake ƙwace iko da fadar shugaban ƙasar da ke Khartoum a ranar Juma’a bayan gwabza yaƙi da rundunar RSF.
Rahotanni daga jihar Borno na cewa wadansu mutane da kawo lokacin rahoton nan ba a san ko su wanene ba sun kwashe kayan abincin wata motar Hukumar abinci ta duniya (WFP) a garin Gubio, yayin da take kan hanyarta ta zuwa Damasak.
Tsohon gwamnan jihar kano kuma shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya ce babu wata gamayyar ’yan adawa da za ta iya hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu lashe wa’adi na biyu a zaɓen 2027 idan Allah ya kai mu.
Majalisar Wakilan Najeriya ta amince da dokar ta baci, da kuma dakatarwar da shugaba Tinubu ya yi wa gwamanan jihar Ribas Siminalayi Fubara cikin yanayi na kusan na bai daya.
Hukumar EFCC ta kama babban Akanta-janar na jihar Bauchi, Alhaji Sirajo Mohammed Jaja, kan zargin almundahanar naira biliyan 70.
Jaridar TRT Hausa ta bayyana cewa Gidan talbijin na Sudan ranar Alhamis ya ce sojojin ƙasar na dab da karɓe iko da Fadar shugaban ƙasar a Khartoum daga hannun dakarun rundunar RSF, lamarin da ya kawo wani babban sauyi a yaƙin da aka yi shekara biyu ana gwabzawa wanda yake barazanar raba ƙasar.
A ranar Talata ne, Shugaba Tinubu ya sanar da sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya bayyana cewa rikicin siyasar jihar yana barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.
Wannan mataki ya janyo ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke ganin hakan bai dace da kundin tsarin mulki ba.
Ƙungiyoyin NLC da TUC sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta janye wannan mataki, don kada ya jefa Najeriya yanayin saɓa wa doka a nan gaba.
Wasu ’yan bindiga sun kai hari Kasuwar Kayan Miya ta Akinyele, kusa da Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, inda suka sace Shugaban Kasuwar, Alhaji Usman Yako.
Asibitin Ƙasa da Asibitin Asokoro da ke Abuja sun cika maƙil da mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar tankar gas da ta auku da daren Laraba a gadar Karu.
Hasashe na bayyana cewa ’yan Najeriya na gabar fuskantar ƙarin farashin man fetur bayan da Matatar Man Dangote ta bayyana cewa ta daina sayar wa ’yan kasuwa man fetur da Naira.