Sojojin Sudan Na Daf Da Kwace Fadar Shugaban Kasa Daga Dakarun RSF – Gidan Talabijin Na Sudan

Jaridar TRT Hausa ta  bayyana cewa Gidan talbijin na Sudan ranar Alhamis ya ce sojojin ƙasar na dab da karɓe iko da Fadar shugaban ƙasar a Khartoum daga hannun dakarun rundunar RSF, lamarin da ya kawo wani babban sauyi a yaƙin da aka yi shekara biyu ana gwabzawa wanda yake barazanar raba ƙasar.

A yammacin ranar Laraba, an yi musayar wuta a kusa da fadar shugaban ƙasar, inda aka ji fashewar abubuwa da kuma hare-haren sama da sojin ta kai tsakiyar Khartoum, kamar yadda shaidu da kamfanin dillancin labaran Reuters suka ruwaito.

Ɓangarorin biyu na soji sun yi juyin mulki a shekarar 2021, lamarin da ya katse shirin miƙa mulki ga farar-hula, kuma yaƙi ya ɓarke a watan Afrilun shekarar 2023 bayan wani sabon shirin miƙa mulki ga farar-hula ya janyo rikici.

Yaƙin ya janyo abin da Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ke kira matsalar jinƙai mafi girma a duniya da kuma ƙeta haƙƙin ɗan’adam mai yawa.

Post masu alaƙa

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 26 a Borno

Tinubu ya tafi hutun mako uku

Rundunar juyin juya halin Iran (IRGC) ta ce wani babban jirgin dakon mai ya kama da wuta tare da tsaya