Sojojin Sudan Na Daf Da Kwace Fadar Shugaban Kasa Daga Dakarun RSF – Gidan Talabijin Na Sudan

Jaridar TRT Hausa ta  bayyana cewa Gidan talbijin na Sudan ranar Alhamis ya ce sojojin ƙasar na dab da karɓe iko da Fadar shugaban ƙasar a Khartoum daga hannun dakarun rundunar RSF, lamarin da ya kawo wani babban sauyi a yaƙin da aka yi shekara biyu ana gwabzawa wanda yake barazanar raba ƙasar.

A yammacin ranar Laraba, an yi musayar wuta a kusa da fadar shugaban ƙasar, inda aka ji fashewar abubuwa da kuma hare-haren sama da sojin ta kai tsakiyar Khartoum, kamar yadda shaidu da kamfanin dillancin labaran Reuters suka ruwaito.

Ɓangarorin biyu na soji sun yi juyin mulki a shekarar 2021, lamarin da ya katse shirin miƙa mulki ga farar-hula, kuma yaƙi ya ɓarke a watan Afrilun shekarar 2023 bayan wani sabon shirin miƙa mulki ga farar-hula ya janyo rikici.

Yaƙin ya janyo abin da Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ke kira matsalar jinƙai mafi girma a duniya da kuma ƙeta haƙƙin ɗan’adam mai yawa.

Post masu alaƙa

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC