Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya shigar da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa (ICPC) sabuwar ƙara ta naira biliyan 10 a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan hana shi ganin iyalansa yayin da hukumar ke tsare da shi.
A cikin ƙarar da lauyansa Ubong Akpan ya shigar ranar 13 ga Agustan 2026, El-Rufai ya ce ICPC ta hana matarsa Aichatou Asabe da ɗansa Abba El-Rufai ziyartarsa, lamarin da ya ce ya tauye masa haƙƙinsa na samun kulawa daga iyalansa.
Ya ce hana shi hulɗa da iyalansa ya hana shi samun abinci, magunguna da sauran muhimman abubuwan da iyalansa za su kawo masa yayin da yake tsare, duk ba tare da wani sahihin dalili na doka ko umarnin kotu ba.
El-Rufai na kuma neman kotu ta ayyana cewa an karya masa haƙƙoƙinsa na ɗanadam da ƙundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada.
Haka kuma yana neman diyyar naira biliyan 10 kan abin da ya bayyana a matsayin take haƙƙinsa.
