Home » Fursunoni 7 Sun Tsere Daga Gidan Yarin Osun

Fursunoni 7 Sun Tsere Daga Gidan Yarin Osun

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Hukumar kula da gidajen yari ta kasa ta bayyana cewa yanzu haka ta fara gudanar da bincike kan wasu fursunoni bakwai da suka tsere daga gidan yarin Ilesa dake jihar Osun.

Hukumar ta ce daurarrun sun tsere ne sakamakon ruwan sama mai karfi da ya lalata wani bangare na gidan yarin.
mai magana da yawun hukumar Umar Abubkar , ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar talata.

A cewarsa, ruwan sama mai karfi ya karya bangon da ke kewaye da gidan yarin, wanda hakan ya ba wa fursunoni damar tserewa.

Shugaban hukumar kula da gidajen yari na kasa, Sylvester Ndidi Nwakuche, ya bayar da umarnin gudanar da bincike cikin gaggawa kan faruwar lamarin, tare da hada kai da hukumomin tsaro domin kamo fursunonin da suka tsere.

 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?