Home » Ma’aikatan KEDCO Za Su Tsunduma Yajin Aiki

Ma’aikatan KEDCO Za Su Tsunduma Yajin Aiki

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Ma’aikatan Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) za su shiga yajin aiki daga daren Talata wayewar garin Laraba, bisa zargin gazawar kamfanin wajen biyan kudaden fansho na ma’aikata.

Kungiyar Ma’aikatan Lantarki ta Kasa (NUEE) reshen shiyyar Kano — wadda ta kunshi jihohin Kano, Jigawa da Katsina — ce ta sanar da hakan a daren Talata.

Babban Sakataren Tsare-Tsaren kungiyar, Comrade Muhammad Babangida Muhammad, ya shaida wa manema labarai .

Ya ce sun dauki matakin ne bayan dogon jinkiri da suka ce KEDCO ta yi wajen biyan hakkokin fanshon ma’aikatan da suka yi ritaya.

“Mun gaji da jira da kuma alkawuran da ba a cika ba. Don haka yajin aikin nan ba zai tsaya ba sai an biya bukatun ma’aikata,” in ji shi.

Yanzu haka, ana sa ran yajin aikin zai shafi samar da wutar lantarki a wasu sassan jihohin da KEDCO ke kula da su.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?