Home » Gwamnatin Kano za ta fara raba wa ɗalibai mata tallafi

Gwamnatin Kano za ta fara raba wa ɗalibai mata tallafi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano ta bayyana cewa ta fara shirin raba Naira dubu ashirin ga dalibai mata dubu arba’in da biyar a matsayin tallafi domin ƙarfafa wa iyaye su riƙa tura ‘ya’yansu makaranta.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ne ya bayyana hakan a yayin gudanar da bikin ranar samun ‘yancin Najeriya karo na sittin da uku da aka yi a Sani Abacha Stadium.

Ya kuma ce za a dawo da motocin da ke kai yara mata zuwa makaranta tare da dawo da su unguwanninsu.

Sannan gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta gina karin makarantu a ƙananan hukumomi 44 da ke jihar nan domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta ko da ke yawa a tituna.

A irin wannan yunƙuri ne, gwamnatin ta shirya aikewa da ɗalibai dubu ɗaya da ɗaya ketare domin yin digiri na biyu da suka samu sakamakon mai daraja ta ɗaya a digirinsu na farko.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?