• Home  
  • Gwamnatin Najeriya ta dakatar da yanke wa jihohi kuɗaɗe kai tsaye daga asusun jihohi
- Labarai

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da yanke wa jihohi kuɗaɗe kai tsaye daga asusun jihohi

Shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF) kuma gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa takwarorinsa bayani a ganawar da suka yi jiya Talata a Abuja.

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da yanke wa jihohi kuɗaɗe kai tsaye daga asusun jihohi

Gwamnatin tarayyar ta amince ta dakatar da yankar kudade daga asusun jihohi a kan bashin London da Paris Club.

Shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya (NGF) kuma gwamnan jihar Sokoto Aminu Tambuwal ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa takwarorinsa bayani a ganawar da suka yi jiya Talata a Abuja.

Haka kuma ya ce ministar kudi ta yi alkawarin tabbatar da ganin an mayarwa da jihohin kudin da aka yanke a baya.

A baya-bayan nan batun yankar kudin na Paris Club ya kasance babban abin takaddama tsakanin gwamnatin tarayyar  da gwamnatin jihohi.

Takardar bayan taron ta kuma nuna cewa an samu sabon shugabanci a kungiyar inda mambobin suka amince ta hanyar sasantawa.

 Gwamnan jihar Kwara, Abdulrahman Abdulrazaq ne ya zama sabon shugaba, yayin da Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya zama mataimaki.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000