Home » Gwamnatin Tarayya za ta kara wa ma’aikatanta albashi

Gwamnatin Tarayya za ta kara wa ma’aikatanta albashi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Gwamnatin Tarayya za ta kara wa ma'aikatanta albashi

A yunkurin shugaban kasa na fara daukar matakan sauya tsarin tafiyar da gwamnati domin samar da daidaton tattalin arziki, yaki da hauhawar farashi, bunkasa ayyukan masana’antu, samar da tsaron rayuka da dukiya, da kuma tallafa wa talakawa da sauran mabukata.

Shugaban ya ce bisa tattaunawarmu da ‘yan kwadago da ‘yan kasuwa da sauran masu ruwa da tsaki, ya amince da fara biyan karin albashi na farko inda za a biya kara mafi karancin albashin gwamnatin tarayya ba tare da kara hauhawar farashi ba.

Karin dai zai zama na tsawon watanni shida ne masu zuwa, inda kananan ma’aikatan Gwamnatin Tarayya za su samu karin Naira Dubu Ashirin da Biyar kowanne wata a albashinsu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?