Home » Hastsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 12 Edo

Hastsarin Mota Ya Yi Ajalin Mutane 12 Edo

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Aƙalla fasinjoji 12 ne suka ƙone ƙurmus a wani mummunan hatsari da ya auku a kan titin Benin zuwa Auchi a Jihar Edo.

Kakakin Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) a Edo, Cyril Mathew, ya tabbatar da aukuwar hatsarin.

Ya ce wata mota ƙirar Toyota Hiace ce ta yi karo da babbar tifa.

A cewarsa, hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5 na asuba a ranar Asabar, a kusa da wani shingen sojoji da ke yankin Igueoviobo.

“Motar ta taso ne daga Zuba a Babban Birnin Tarayya tana kan hanyarta n zuwa Benin, amma ta yi karo da wata babbar tifa da ke kan hanyar zuwa Auchi.

“Duk fasinjojin da ke cikin motar sun rasa rayukansu,” in ji shi.

Mathew, ya ce ana zargin direban motar da gajiya yayin tuƙi, lamarin da ya sa ya fara barci a kan hanya, wanda hakan ya haddasa hatsarin.

Karon da motocin suka yi ya haddasa tashin wuta, lamarin da ya sanya fasinjojin zuka ƙone ƙurmus.

Sai dai direban babbar tifar da yaronsa sun tsira ba tare da sun ji rauni ba.

Kakakin ya shawarci direbobi da suke hutawa a duk lokacin da suka gaji domin gujewa aukuwar hatsari.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?