Home » Hukumar RaYa Al’adu Ta Najeriya Za Ta Kaddamar Da Kirkirarriyar Fasahar Zamani

Hukumar RaYa Al’adu Ta Najeriya Za Ta Kaddamar Da Kirkirarriyar Fasahar Zamani

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar Raya Al’adu Ta Najeriya (National Troupe of Nigeria) a karkashin jagorancin Kaltume Bulama Gana, FSNA, na shirin  wani gagarumin taro domin kaddamar da kirkirarriyar fasahar zamani da zimmar karfafawa yara da matasa guiwa wurin kallo da sauraron wakoki, kade-kade da raye-rayen gargajiya. 

Taron na National Troupe of Nigeria zai gudana ne a lambun hutun Queen Amina da ke Iganmu Jihar Legas ranar Asabar 21 ga Disamba 2024. 

Sabon shirin zai kawo cigaba da ba a taba ganin irinsa ba, wanda zai baiwa mutane daga kowane lungu da sako na duniya damar ganin kyawawan  al’adun Najeriya.

National Troupe of Nigeria na ganin cewa wannan yunkuri zai bai wa matasa damar sanin kyawawan al’adunsu na asali a matsayinsu na cikakkun ‘yan Najeriya. 

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?