Home » Malam Uba Sani Ya Mayarwa Iyalan Abacha Filayen Da El Rufai Ya Karbe

Malam Uba Sani Ya Mayarwa Iyalan Abacha Filayen Da El Rufai Ya Karbe

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya mayar wa iyalan tsohon shugaban kasa Janar Sani Abacha filayen su guda 2 da tsohon gwamna Nasir El Rufai ya kwace a lokacin mulkinsa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewar lauyan iyalan tsohon marigayin shugaban kasar Reuben Atabo ne ya bayyana haka ga manema labarai.

Sanarwar gwamnatin jihar Kaduna da Babban Daraktar ma’aikatar kula da filaye Mustapha Haruna ya gabatar tace, Gwamna Uba Sani ya rubutawa iyalan Janar Abacha wasika wanda aka sanya sunan Mohammed Sani Abacha, yana mai bayyana mayar musu da filayen da kuma gabatar musu da bukatar cewar su je su biya harajin da aka saba karba a hannun su na mallakar filayen.

An ce A shekarar 2022 ne dai tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru El Rufai ya gabatar da sanarwa a jarida ranar 28 ga watan Afrilu inda aka bayyana kwace filayen tare da soke takardun wadanda aka mallakawa a farko.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?