Home » Kalaman Da Wani Limami Ya Furta Kan Dokta Idris Dutsen Tanshi Sun Haifar Da Rudani

Kalaman Da Wani Limami Ya Furta Kan Dokta Idris Dutsen Tanshi Sun Haifar Da Rudani

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Kwamishinan ƴansandan jihar Bauchi a Najeriya, Sani-Omolori Aliyu ya yi kira ga ƴan jihar da su kwantar da hankalinsu kan hargitsin da aka samu a wani masallaicin jihar kan batun marigayi Sheikh Abdulaziz Idris Dutsen Tanshi.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar, ya ce, “a ranar 4 ga Afriku ne wasu suka kai ƙarar cewa limamin masallacin Galli da ke Jahun, Ahmad Isa Jaja a cikin hudubarsa ya faɗa wasu kalamai game da Marigayi Malam Abdulaziz Idris da ba su yi wa ɗalibansa daɗi, inda suka taru a masallaci domin nuna rashin daɗinsu.”

Sanarwar ta ce hakan ya sa kwamishinan ƴansandan jihar Sani-Omolori Aliyu, ya tura jami’ai na musamman domin tabbatar da kaucewa tayar da zaune tsaye.

“Da jami’anmu suka isa masallacin, sun samu nasarar tseratar da limamin da fatattakar wadanda suka taru cikin ƙwarewa, sannan kwamishinan ƴansanda ya yi umarni a ƙaddamar da bincike domin gano musabbabin lamarin,” in ji sanarwar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?