Home » Kano: Ƙungiyar ‘Yan Jaridu, NUJ, Ta Taya Abba Kabir Yusuf Murna Lashe Zaɓe

Kano: Ƙungiyar ‘Yan Jaridu, NUJ, Ta Taya Abba Kabir Yusuf Murna Lashe Zaɓe

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Ƙungiyar ‘Yan Jarida ta Ƙasa, reshen jihar Kano, ta taya zaɓaɓɓen Gwamnan jihar na jam’iyyar NNPP, Abba Kabir Yusuf murnar samun nasara a zaɓen Gwamnan da aka gudanar.

Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Shugaban ƙungiyar Kwamared Abbas Ibrahim, ta tabbatar da cewa Abban zai kai jihar matakin ci gaba ta fuskar ayyukan raya ƙasa da ci gaban al’umma, duba da ƙwarewar da yake da ita da kuma kasancewarsa Injiniya.

Daga ƙarshe kuma ƙungiyar ‘yan jaridun ta yi addu’ar Allah ya yi riƙo da hannun zaɓaɓɓen Gwamnan, kuma ta yi fatan harkar yaɗa labarai  ta sami tagomashi a sabuwar gwamnatin.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?