Home » Kungiyar Kwadago Ta Koka Kan Dakatar da Albashin Ma’aikata 10,000 da Gwamnatin Kano Ta Yi

Kungiyar Kwadago Ta Koka Kan Dakatar da Albashin Ma’aikata 10,000 da Gwamnatin Kano Ta Yi

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Kungiyar Kwadago Ta Koka Kan Dakatar da Albashin Ma'aikata 10,000 da Gwamnatin Kano Ta Yi

Kungiyar Kwadago ta ƙasa reshen jihar Kano ta magantu kan matsalar Ma’aikata akalla 10,000 da gwamnatin jihar Kano ta tsayar musu albashi.

Idan za’a iya tunawa, a ƴan kwanakin baya ne, gwamnan jihar Kano, engr. Abba Kabir Yusuf ya ba da umarnin tsayar da albashin ma’aikata da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya dauka.

Shugaban kungiyar na jihar kano, Kabiru Inuwa ya bayyana cewa za su gudanar da wata ganawa don samo mafita a kan matsalar.

Shugaban ya bayyana cewar za su samo mafita a kan wanna matsala a ganawar da za su yi a ranar Litinin.  

Haka kuma a yayin tattaunawar, wadanda abin ya shafa za su rubuto matsalolinsu ga kungiya don nemo mafita.

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ce sun dakatar da biyan albashin ma’aikatan har sai lokacin da aka gama tantance su.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?