• Home  
  • Mata Za Su Yi Zanga-zanga Tsirara A Majalisar Dokokin Najeriya
- Babban Labari - Labarai

Mata Za Su Yi Zanga-zanga Tsirara A Majalisar Dokokin Najeriya

Wasu Mata magoya bayan Sanata Muhammad Ali Ndume sun yi barazanar yin zanga-zanga tsirara a Majalisar Dokoki ta Kasa, idan ba a mayar da shi kan shugabancin kwamitocin Majalisar Dattawa ba. Magoya bayan sanatan sun yi wannan barazana ne a lokacin da Ndume ya karbi bakuncinsu tare da sauran magoya bayansa a gidansa da ke […]

Wasu Mata magoya bayan Sanata Muhammad Ali Ndume sun yi barazanar yin zanga-zanga tsirara a Majalisar Dokoki ta Kasa, idan ba a mayar da shi kan shugabancin kwamitocin Majalisar Dattawa ba.

Magoya bayan sanatan sun yi wannan barazana ne a lokacin da Ndume ya karbi bakuncinsu tare da sauran magoya bayansa a gidansa da ke Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

A yayin taron ne Sanata Ali Ndume ya bayyana sharadinsa na ci gaba da zama a Jam’iyyarsa ta APC.

A kwanakin baya ne dai uwar Jami’yyar APC na da hannu wajen tsige Ndume daga mukaminsa a Majalisar saboda ya soke Gwamnatin Shugaba Tinubu kan yunwa da tsadar rayuwa da ake fama da su a Najeriya.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai