Home » An Tsaurara Matakai A Iyayakokin Najeriya Saboda Zanga-zanga

An Tsaurara Matakai A Iyayakokin Najeriya Saboda Zanga-zanga

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamnatin Najeriya ta dauki matakan tsaurara tsaro a iyakokin kasar gabanin zanga-zanga da ake shirin farawa ranar Alhamis ga watan Agusta, 2024. 

Shugabar Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa Kemi Nandap, ta ce an tsaurara matakan tsaro a dukkanin iyakokin Najeriya

Jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Kenneth Udo ne ya bayyana hakan a  wata sanarwar da ya fitar a madadin hukumar ranar Asabar. 

Kwanturola Janar Kemi Nandap, ta umarci dukkanin shugabannin shiyya-shiyya a Najeriya su yi hattara.

Nandap ta bukaci hukumar su ƙara sanya ido kan zanga-zangar da wasu ke shirin yi a Najeriya

Shugabar Hukumar ta kuma ce umarnin na da nufin tabbatar da cewa wasu ‘yan ƙasashen waje ba su shigo cikin ƙasar domin shiga zanga-zangar ba.

“Ta wannan hanyar ce za a tabbatar da cewa babu wani baƙon da zai iya fakewa da zanga-zangar don tada zaune tsaye a ƙasar nan,” in ji ta.

Domin tabbatar da cewa ba a samu wata matsala dangaen da wannan aiki ba, hukumar ta dakatar da dukkanin hutun wucin gadin jami’anta domin tabbatar da ba a samu matsala ba a lokacin zanga-zangar.

Kemi Nandap, ta tabbatar wa daukacin ’yan Najeriya shirin hukumar na kiyaye iyakokin ƙasar domin inganta tsaro.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?