Home » Naja’atu da Bafarawa Sun kafa Sabuwar Tafiyar Matasa

Naja’atu da Bafarawa Sun kafa Sabuwar Tafiyar Matasa

by Mubarak Ibrahim Mandawari
0 comment

Tsohon gwamnan jihar Sakkwato Attahiru Bafarwa da kuma fitacciyar ‘ƴar gwagwarmaya a Arewacin Najeriya, Hajiya Naja’atu Muhammad, sun ƙaddamar da wata sabuwar tafiyar matasa don ceto yankin Arewacin Najeriya me suna Northern Star Youth Movement Initiative (NSYMI).

A jawabinsa, Bafarawa wanda tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa ne a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, ya ce, lokaci ya yi da matasa za su karɓi jagoranci. Idan aka basu dama, za su taka rawar gani, a cewar Bafarawa, ya kuma ƙara da cewa ƙungiyar na Shirin buɗe ofisoshi a faɗin ƙasar nan.

A ranar Talata ne manyan ƴan siyasar Arewan suka ƙaddamar da tafiyar matasan da nufin tallafawa matasa,da kuma ɓullo da hanyoyin magance matsalolin da suka dabaibaye yankin.

A nata ɓangaren, Hajiya Naja’atu Mohammed, ta jaddada cewa ƙungiyar ba ta siyasa ba ce, ta mayar da hankali ne kawai wajen tallafa wa matasa da kuma kawo cigaban yankin Arewacin Najeriya.

“Manufarmu a fili take, amfani da ƙarfi da kuma basirar da Allah Ya yi wa kowane ɗan Arewa domin kawo cigaban rayuwa da na tattalin arziki a yankin,” in ji Hajiya Naja’atu.

A watannin baya dai an kafa wata makamanciyar wannan tafiyar da aka kira da “The Youth Movement,” wato tafiyar matasa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?