Home » Nijar Ta Amince da Ƙawancen Mali Domin Yaƙi da ‘Yan Ta’adda

Nijar Ta Amince da Ƙawancen Mali Domin Yaƙi da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Mali da Nijar sun amince a farkon watan nan cewa su yi aiki tare domin murƙushe ƙungiyoyin da ke da alaƙa da Al-Qaeda da IS.

Sannan Shugaban ƙasar Nijar, Muhammad Bazoum ya naɗa sabon babban hafsan dakarun sojin ƙasar, daidai lokacin da Nijar ke fafutukar murƙushe ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

Kawo yanzu, gwamnati ba ta yi bayani a kan dalilan maye gurbin Janar Salifou Mody da Janar Abdou Sidikou Issa ba, wanda a baya ya riƙe manyan muƙamai a ɓangaren na sojoji.

Akwai ƙungiyoyi da dama na masu iƙirarin jihadi a Nijar ciki har da Boko Haram wadda ta samo asali daga Najeriya mai maƙwabtaka.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?