• Home  
  • Nijar Ta Amince da Ƙawancen Mali Domin Yaƙi da ‘Yan Ta’adda
- Labarai

Nijar Ta Amince da Ƙawancen Mali Domin Yaƙi da ‘Yan Ta’adda

Sannan Shugaban ƙasar Nijar, Muhammad Bazoum ya naɗa sabon babban hafsan dakarun sojin ƙasar, daidai lokacin da Nijar ke fafutukar murƙushe ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

Mali da Nijar sun amince a farkon watan nan cewa su yi aiki tare domin murƙushe ƙungiyoyin da ke da alaƙa da Al-Qaeda da IS.

Sannan Shugaban ƙasar Nijar, Muhammad Bazoum ya naɗa sabon babban hafsan dakarun sojin ƙasar, daidai lokacin da Nijar ke fafutukar murƙushe ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi.

Kawo yanzu, gwamnati ba ta yi bayani a kan dalilan maye gurbin Janar Salifou Mody da Janar Abdou Sidikou Issa ba, wanda a baya ya riƙe manyan muƙamai a ɓangaren na sojoji.

Akwai ƙungiyoyi da dama na masu iƙirarin jihadi a Nijar ciki har da Boko Haram wadda ta samo asali daga Najeriya mai maƙwabtaka.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000