Gwamnatin Nijar ta soke lasisin kamfanonin sufuri sama da talatin da kuma na direbobin manyan motoci, sakamakon ƙin yarda su kai mai zuwa makwabciyar ƙasar Mali bisa dalilan tsaro.
Ƙungiyar JNIM, wadda ke da alaƙa da al-Qaeda, ta kakaba takunkumin hana shigar da mai cikin ƙasar Mali, abin da ya janyo mummunan ƙarancin mai tun daga watan Satumba.
Lamarin ya shafi harkokin sufuri da kasuwanci da rayuwar yau da kullum a ƙasar.
A watan Nuwamba, Nijar ta samu nasarar tura tankokin mai har guda 82 zuwa Mali, ƙarƙashin rakiyar sojoji.
Sai dai duk da wannan yunƙuri, mayaƙan masu iƙirarin jihadi sun ci gaba da kai hare-hare kan ayarin motocin da ke ƙoƙarin shigar da man, abin da ya ƙara tsoratar da direbobi da kamfanonin sufuri.
Rahotanni sun nuna cewa ƙungiyar JNIM na kai hare-hare kan motocin mai ne a matsayin wani ɓangare na yunƙurinta na raunana gwamnatocin yankin.
- Ƴan sanda sun kama dillalin miyagun kwayoyi da wasu Mutane 5 a Kano
- Ƴan sanda sun kama dillalin miyagun kwayoyi da wasu Mutane 5 a Kano
Sakamakon ƙarancin man, filin jirgin saman Bamako ya soke tashin wasu jirage a ‘yan kwanakin nan.
Nijar, Mali da Burkina Faso duk ƙasashe ne da ke ƙarƙashin mulkin sojoji bayan juyin mulki, kuma sun haɗa kai a ƙarƙashin ƙungiyar haɗin kan ƙasashen yankin Sahel AES.
Ƙasashen sun kuma nisanta kansu daga ƙungiyar ECOWAS, yayin da suke fuskantar ƙalubalen tsaro da na tattalin arziƙi a yankin Sahel.
