Home » Shugaban Ƙasa Mai Jiran Gado Ya Musanta Wani Zargi da Ake Masa

Shugaban Ƙasa Mai Jiran Gado Ya Musanta Wani Zargi da Ake Masa

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Zaɓabben shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya musanta rahotannin da ke cewa ya gana da babban Jojin Najeriya a birnin London na ƙasar Ingila.

Wata sanarwa da ta samu sa hannun daraktan yaɗa labaru na kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bayo Onanuga, ta bayyana labarin a matsayin ƙage maras tushe.

A cikin kwanakin nan ne wasu jaridu da kuma masu amfani da shafukan sada zumunta suka rinka yaɗa labarin yadda aka yi wata ganawar sirri, tsakanin Bola Ahmed Tinubu da babban Jojin Najeriya, Olukayode Ariwoola.

Labarin ya nuna cewa babban Sojin ya yi ɓadda-bami ta hanyar hawa keken guragu domin ganawa da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar a birnin London.

Sai dai sanarwar, wadda aka fitar ta ce an ƙirƙiri labarin ne domin sanya shakku a zukatan ƴan Najeriya game da nasarar da jam’iyyar APC ta samu a zaɓen da ya gabata.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?