‘Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-hare A Kano
Gamayyar hukumomin tsaro a jihar Kano sun gargadi mutane da su kaucewa wuraren cunkoson jama’a sakamakon samun bayanan sirri kan yunkurin kawo hare-hare jihar da wasu yan ta’adda ke shirya wa.
Gamayyar hukumomin tsaro a jihar Kano sun gargadi mutane da su kaucewa wuraren cunkoson jama’a sakamakon samun bayanan sirri kan yunkurin kawo hare-hare jihar da wasu yan ta’adda ke shirya wa.
Ana zargin wata ɗaliba a kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar Kano, da sa samarin ta su yi wa wani malaminsu mai suna Aliyu Hamza Abdullahi dukan kawo wuƙa.
Tsohon gwamnan jihar Kano kuma Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Dokta Abdullahi Umar Ganduje, ya ce dole sojoji su mamaye dazuka domin kawo ƙarshen ’yan bindiga a Najeriya.
Abdulmumin Jibrin Kofa Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kiru da Bebeji dags Jihar Kano, ya ce za su yi duk mai yiwuwa domin ganin sun kawo ƙarshen rashin jituwar da ke tsakanin manyan ’yan siyasar jihar biyu, Dokta Rabiu Musa Kwanwaso da Dokta Abdullahi Umar Ganduje.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta samu nasarar kama wasu mutane 6 da ake zargin sun addabi sassan birnin da sace-sacen wayoyin fasinjoji, tare da kwato baburan adaidaita sahu 2 da kuma wayoyin sata 15.
Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano, ta bayyana cewa ta gurfanar da Shamsiya Adamu a gaban kotu bayan sake kama karin mutane 4 da kwato wayoyin sata 12 da ake zargin suna cikin gungun mutanen da ta ke jagoranta wurin sata da damfarar jama’a.
Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da shirin hada gwiwa da bankin cigaban Musulunci (IDB) domin samar da makarantu guda hudu da za a rika koyarwa da harshen Ingilishi da kuma Larabci.
Rundunar ‘yan sandan jihar kano ta gurfanar da daya daga cikin matasan da ake zargi da kashe wani dan sanda, mai suna Murtala Auwalu, a kan titin france road lokacin da yake tsaka da gudanar aiki, a ranar 1 ga watan Janairun 2025.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta gurfanar da wasu matasa hudu a gaban kotun majistiri mai lamba 43, dake zaman ta a unguwar Gyadi-gyadi, karkashin jagorancin mai shari’a Kabiru Sallau, bisa zarginsu da aikata laifuka hudu.
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya roki gwamnatin tarayya da ta rage kudin aikin Hajjin bana, duba da irin kalubalen da ‘yan kasa ke fuskanta na tattalin arziki.