NDC

Ɗan Kwankwaso ya zama ɗan takarar Mataimakin Gwamnan Kano a NDC

Ɗan takarar gwamnan Jihar Kano a jam’iyyar NDC, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya zaɓi Mustapha Rabiu Musa Kwankwaso, ɗan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a matsayin abokin takararsa na mataimakin gwamna a Zaɓen 2027. Mustapha Kwankwaso, wanda tsohon Kwamishinan Matasa da Wasanni ne a gwamnatin Abba Kabir Yusuf, ya yi murabus daga muƙaminsa, inda ya koma tafiyar […]

Read more

Ɗan Ganduje Ya Sayi Fom Ɗin Takarar Majalisar Tarayya A NDC

Abdulaziz Umar Ganduje, babban ɗan tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya sayi fom ɗin takarar kujerar Majalisar Tarayya a ƙarƙashin jam’iyyar NDC. Zai tsaya takarar ne a mazaɓar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado da ke Jihar Kano. Duk da kasancewar mahaifinsa a jam’iyyar APC, Abdulaziz, ya daɗe yana bin siyasar Kwankwasiyya kuma yana […]

Read more

Jam’iyyar NDC na gudanar da babban taronta na ƙasa

Jam’iyyar hamayyar ta NDC a Najeriya na gudanar da babban taronta na ƙasa domin zaɓen sabbin shugabanninta. Matakin na zuwa ne mako guda bayan da manyan jiga-jigan siyasar ƙasar biyu, Peter Obi da Kwankwaso suka sanar da komawa cikinta. Ɗaruruwan magoya bayan jam’iyyar ne suka taru a harabar wurin gudanar da taron a Abuja. Akwai […]

Read more